![]() |
Arbeen Tahir bayan kammala rubuta Alkur'ani Hoto: Press TV |
Wata karamar yarinya, Arbeen Tahir daga kauyen Hajin na gundumar Bandipora ta arewacin Kashmir ta haddace tare da rubuta Alkur'ani mai girma.
A wata wallafa da shafin Press TV suka fitar, sun bayyana yarinyar tun tana karamarta taci alwashin rubuta littafi mai tsarkin, bisani ta kammala cikin nasara.
Da ake bayyana maganar yarinyar ta ce; "buri na ne tun ina karama, na rubuta Alkur'ani".
Fasihiyar yarinyar ta rubuta cikakken Alkur'ani cikin watannk 6, cikin shafuka dari tara, kamar yadda Press TV ta rawaito.
