Tun da sanyin safiyar yau Alhamis ne, jami'an tsaro suka tare dukkan hanyoyin zuwa babbar kotun musulunci ta jihar Kano inda za a yanke hukunci a shari'ar da gwamnatin Kano ta gurfanar da Sheikh Abduljabar Nasiru Kabara game da zarge-zargen batanci da ake yi masa. Mai Shari'a Alkali Ibrahim Sarki Yola ne zai yanke hukuncin.
Shaikh Abduljabbar din dai tuni ya iso kotu.

