Ƴan sanda a Kano sun cafke matasa 61 bisa zargin su da ƙwace wayoyi a taron Tinubu

 

Source details from Police 

Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta yi holin wasu matasa su 61 da ta cafke bisa zargin su da ayyukan ta’addanci ta hanyar ƙwacen wayoyin mutane a ranar Larabar makon nan.


Rundunar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ta SP Abdullahi Haruna, ya fitar a daren Alhamis ɗin nan.


Kazalika, sanarwar ta ce, an cafke matasan ne ɗauke da makamai da miyagun ƙwayoyi yayin gudanarda taron bada tutar ƴan takarar jam’iyyar APC a filin wasa na Sani Abacha da ke Ƙofar Mata.

Post a Comment

Previous Post Next Post