Qatar 2022: Kocin Brazil ya ajiye aiki bayan wankan Jego da Crotia ta yi mata


Kocin kasar Brazil, Adenor Leonardo Bacchi da aka sani da Tite, ya ajiye aikinsa na horar da tawagar ’yan wasan kasar bayan rashin zuwa matakin kusa da na Karshe a Gasar Kofin duniya da ke gudana a kasar Qatar.

Tite Mai shekaru 61, ya ajiye aikinsa ne jim kadan bayan Crotia ta doke Brazil a bugun fanareti a wasan Kwata-Fainal da suka buga a yammacin jiya Juma’a.
Kasar Crocatia dai ta fitar da Japan a zagayen ’Yan 16 a bugun fanareti, sannan ta maimaita irin wannan nasara a karawarta da Brazil a yammacin ranar Juma’a.

A shekarar 2016 ne dai Tite ya karbi Jagorancin ragamar horar da tawagar ’yan wasan, inda ya jagorance ta wajen lashe Gasar Copa America a shekarar 2019.

Post a Comment

Previous Post Next Post